Man zaitun na gwauruwa
1 Matar wani daga ƙungiyar annabawa ta yi wa Elisha kuka ta ce, "Mijina, bawanka, ya mutu, ka kuma san yadda ya girmama Ubangiji. Amma ga shi yanzu mai binsa bashi ya zo yă kwashe ’ya’yana maza biyu su zama bayinsa."
2 Elisha ya amsa mata ya ce, "Me kike so in yi miki? Ki faɗa mini, me kike da shi a gidanki?"
Sai ta ce, "Baiwarka ba ta da kome a can, sai ɗan tulun man zaitun."
3 Elisha ya ce, "Ki je wurin dukan maƙwabtanki, ki nemi tulunan da babu kome a ciki. Kada ki nemo kaɗan kawai. 4 Sa’an nan ki shiga ciki, ki kulle ƙofar da ke da ’ya’yanki kuke ciki. Ku ɗuɗɗura man a dukan tulunan, sa’ad da kowanne ya cika, sai ki ajiye a gefe."
5 Ta tashi ta shiga tare da ’ya’yanta maza, suka kulle ƙofa. ’Ya’yanta suka kawo mata tuluna, ita kuma tana ɗurawa. 6 Da dukan tulunan suka cika, sai ta ce wa ɗanta, "Kawo mini wani tulu."
Amma ya amsa ya ce, "Ai, ba saura." Sa’an nan man ya daina zuba.
7 Sai ta tafi ta faɗa wa mutumin Allah. Shi kuwa ya ce mata, "Tafi, ki sayar da man, ki biya bashinki. Ki biya bukatanki da na ’ya’yanki da sauran da ya rage."