17 "Allah ya ce, ‘A kwanakin ƙarshe,
zan zubo Ruhuna bisa dukan mutane.
’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci,
samarinku za su ga wahayoyi,
dattawanku kuma za su yi mafarkai.
18 Kai, har ma a kan bayina, maza da mata,
zan zubo Ruhuna a waɗancan kwanaki,
za su kuwa yi annabci.
19 Zan nuna abubuwan banmamaki a sararin sama
da alamu a nan ƙasa,
jini da wuta da kuma hauhawan hayaƙi.
20 Za a mai da rana duhu,
wata kuma ya zama jini,
kafin zuwa rana mai girma da kuma ta ɗaukaka ta Ubangiji.
21 Kuma duk wanda ya kira
bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.’2.21 Yow 2.28-32