25 To, tsaye kusa da gicciyen Yesu kuwa akwai mahaifiyarsa, tare da ’yar’uwar mahaifiyarsa, Maryamu matar Kilofas, da kuma Maryamu Magdalin. 26 Sa’ad da Yesu ya ga mahaifiyarsa a can, da kuma almajirin nan da yake ƙauna tsaye kusa, sai ya ce wa mahaifiyarsa, "Mace, ga ɗanki," 27 ga almajirin kuwa ya ce, "Ga mahaifiyarka." Tun daga wannan lokaci fa almajirin nan ya kai ta gidansa.