4 Bilatus kuwa ya sāke fitowa ya ce wa Yahudawa, "Ga shi, zan fito muku da shi don ku san cewa ban same shi da wani abin zargi ba." 5 Sa’ad da Yesu ya fito sanye da rawanin ƙayar da kuma riga mai ruwan shunayya, sai Bilatus ya ce musu, "Ga mutumin!"
6 Nan da nan da manyan firistoci da ma’aikatansu suka gan shi, sai suka yi ihu suka ce, "A gicciye! A gicciye!"
Amma Bilatus ya amsa ya ce, "Ku, ku ɗauke shi ku gicciye. Ni dai ban same shi da wani abin zargi ba."