14 Da ta faɗin haka, sai ta juya ta ga Yesu tsaye, sai dai ba tă gane cewa Yesu ne ba.
15 Sai ya ce, "Mace, don me kike kuka? Wa kike nema?"
Ta yi tsammani shi ne mai aikin lambun, sai ta ce, "Ranka yă daɗe, in kai ne ka ɗauke shi, gaya mini inda ka ajiye shi, in je in ɗauke shi."
16 Yesu ya ce mata, "Maryamu."
Sai ta juya wajensa ta ɗaga murya ta ce da Arameyanci, "Rabboni!" (Wanda yake nufin "Malam").