Yesu ya sāke tabbatar da Bitrus
15 Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, "Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?"
Ya ce, "I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka."
Yesu ya ce, "Ciyar da ’ya’yan tumakina."
19 Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, "Bi ni!"