46 Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum. 47 Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
48 Yesu ya ce masa, "Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya."
49 Ma’aikacin hukuman ya ce, "Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu."
50 Sai Yesu ya amsa ya ce, "Ka tafi. Ɗanka zai rayu."
Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi. 51 Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa. 52 Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, "Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai."
53 Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, "Ɗanka zai rayu." Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
54 Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.