3 sai ’yan’uwan Yesu suka ce masa, "Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi. 4 Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya." 5 Domin ko ’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.