Pular para o conteúdo
Publicidade

Lucas 8

Yesu ya kwantar da ruwa da iska

22 Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, "Mu haye zuwa wancan gefen tafkin." Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya. 23 Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.

24 Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, "Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!"

Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit. 25 Sai ya tambayi almajiransa, "Ina bangaskiyarku?"

A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, "Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?"

Warkar da mai aljanu

26 Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.

Veja também