16 Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne. 17 Yesu ya ce, "Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane." 18 Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.