10 a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, "Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?"
11 Ya ce musu, "In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba? 12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci."
13 Sa’an nan ya ce wa mutumin, "Miƙa hannunka." Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.