14 A kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa,
" ‘Za ku yi ta ji amma ba za ku taɓa ganewa ba;
za ku yi ta kallo amma ba za ku taɓa gani ba.
15 Gama zuciyar mutanen nan ta taurare;
da ƙyar suke ji da kunnuwansu,
sun kuma rufe idanunsu.
Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu,
su kuma ji da kunnuwansu,
su gane a zuciyarsu,
su kuwa juya, in kuma warkar da su.’ 13.15 Ish 6.9,10