17 To, ka gaya mana, a ra’ayinka? Ya dace a biya Kaisar haraji ko a’a?"
18 Amma Yesu da yake ya san mugun nufinsu, sai ya ce, "Ku munafukai, don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? 19 Ku nuna mini kuɗin da ake biyan haraji da shi." Sai suka kawo masa dinari, 20 sai ya tambaye su ya ce, "Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne?"
21 Suka amsa, "Na Kaisar ne."
Sai ya ce musu, "Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah."