Pular para o conteúdo
Publicidade

Mateus 4

Gwajin Yesu

1 Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis gwada shi. 2 Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa. 3 Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, "In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi."

4 Yesu ya amsa ya ce, "A rubuce yake cewa, Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.4.4 M Sh 8.3"

5 Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali. 6 Ya ce, "In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake,

" Zai umarci mala’ikunsa game da kai,

za su tallafe ka da hannuwansu,

don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.4.6 Zab 91.11,12"

7 Yesu ya amsa masa ya ce, "A rubuce yake kuma cewa, Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.4.7 M Sh 6.16"

8 Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu. 9 Ya ce, "Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada."

10 Sai Yesu ya ce masa, "Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.4.10 M Sh 6.13"

11 Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.

Veja também