Publicidade

Mateus 6

9 "To, ga yadda ya kamata ku yi addu’a.

" Ubanmu wanda yake cikin sama,

a tsarkake sunanka,

10 mulkinka zo

a aikata nufinka a duniya

kamar yadda ake yi a sama.

11 Ka ba mu yau abincin yininmu.

12 Ka gafarta mana laifofinmu,

kamar yadda mu ma muke gafarta wa masu yin mana laifi.

13 Kada ka bari a kai mu cikin jarraba,

amma ka cece mu daga mugun nan. 6.13 Ko kuwa daga mugu ; waɗansu rubuce-rubucen hannun da ba su jima ba ɗaya, gama mulki da iko da ɗaukaka naka ne har abada. Amin.

Veja também

Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-07-05_19-25-13-