Faɗi 16
19 Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima,
ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20 Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa
ko masu haɗama kansu da abinci,
21 gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta,
gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
Faɗi 17
22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai,
kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.