32 Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali;
duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
33 Dūka da kunya ne za su zama rabonsa,
kuma kunyarsa za tă dawwama.
34 Gama kishi kan tā da hasalar miji,
kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
35 Ba zai karɓi duk wata biya ba;
zai ƙi cin hanci, kome yawansu.