11 Sai Ubangiji ya ce, "Fita ka tsaya a kan dutse a gaban Ubangiji, gama Ubangiji yana shirin wucewa."
Sai ga babbar iska mai ƙarfi ta tsage duwatsu, ta kuma ragargaza duwatsu a gaban Ubangiji, amma Ubangiji ba ya cikin iskar. Bayan iskar sai aka yi girgizar ƙasa, amma Ubangiji ba ya cikin girgizar ƙasa.