Pular para o conteúdo
Publicidade

1 Sarakuna 1

Adoniya ya naɗa kansa Sarki

1 Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa. 2 Saboda haka bayinsa suka ce masa, "Bari mu nemi wata budurwa wadda za yi wa ranka daɗe, sarki hidima, kuma kula da shi. Za dinga kwanta kusa da ranka daɗe, ji ɗumi."

3 Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki. 4 Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.

5 Adoniya,1.5 Adoniya shi ne ɗa na huɗu na Dawuda (2Sam 3.4) kuma yana da shekara 35 da haihuwa. Amnon, Absalom, da Kileyab (da ya mutu yana yaro) duk sun mutu. wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, "Zan zama sarki." Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa. 6 (A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa ce, "Me ya sa kake yin haka ba?" Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)

7 Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya1.7 Zeruhiya ’yar’uwar Dawuda ce da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya. 8 Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi1.8 Ko kuwa da abokansa da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.

9 Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci yan’uwansa, wato, sauran ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda, 10 amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.

11 Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, "Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka daɗe, sarkinmu Dawuda ba? 12 Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon. 13 Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, Ranka daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, "Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, kuma zauna a kujerar sarautar ba"? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?14 Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa."

15 Saboda haka Batsheba ta je don ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima. 16 Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki.

Sai sarki ya tambaye ta ya ce, "Me kike so?"

17 Ta ce masa, "Ranka daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.18 Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba. 19 Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba. 20 Ranka daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka daɗe sarkina, a bayanka. 21 In ba haka, bayan an binne ranka daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi."

22 Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso. 23 Sai aka faɗa wa sarki, "Ga annabi Natan." Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.

24 Natan ya ce, "Ranka daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, kuma zauna a kujerar sarautarka? 25 Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, Ran Sarki Adoniya daɗe!26 Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba. 27 Ranka daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka daɗe, sarki ba?"

Dawuda ya naɗa Solomon Sarki

28 Sai Dawuda ya ce, "Kira Batsheba shiga." Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.

29 Sai sarki ya yi rantsuwa, "Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa, 30 tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona."

31 Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, "Bari ran Sarkina Dawuda daɗe, har abada!"

32 Sarki Dawuda ya ce, "Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada." Da suka zo gaban sarki, 33 sai ya ce musu, "Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon. 34 A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, Ran Sarki Solomon daɗe!35 Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo zauna a kujera sarautata, yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda."

36 Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, "Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka daɗe sarkina, tabbatar da haka. 37 Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka daɗe, sarki, haka ma bari kasance da Solomon, kuma mai da kujerar sarautarsa fi kujerar sarautar ranka daɗe, Sarki Dawuda, girma!"

38 Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon. 39 Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa "Ran Sarki Solomon daɗe!" 40 Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.

41 Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, "Me ya jawo surutu haka a birni?"

42 Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, "Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne."

43 Yonatan ya ce wa Adoniya, "A ina! Ranka daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki. 44 Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki, 45 Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan. 46 Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu. 47 Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, Bari Allahnka sa sunan Solomon zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa fi taka girma!Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa 48 ya ce, Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’ "

49 A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse. 50 Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe. 51 Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, "Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, Bari Sarki Solomon rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’ "

52 Solomon ya amsa ya ce, "In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu." 53 Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, "Tafi gidanka."

Estes versículos te tocaram? Ore agora!

+581 estão orando agora.

Junte-se à corrente de oração.

Veja também