16 Sai annabin ya ce, "Kada ka ji tsoro, waɗanda suke tare da mu sun fi waɗanda suke tare da su."
17 Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, "Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa yă gani!" Sai Ubangiji ya buɗe idanun bawan, ya duba, ya ga tuddai cike da dawakai da keken yaƙin wuta kewaye da Elisha.