10 Ko ma a sa’ad da muke tare da ku, mun ba ku wannan umarni cewa, "In mutum ya ƙi yin aiki, kada a ba shi abinci."
11 Mun ji cewa waɗansunku suna zaman banza. Ba sa aikin kome; sai shisshigi kurum. 12 Irin waɗannan mutane muna ba da umarni muna kuma gargaɗe su cikin Ubangiji Yesu Kiristi su natsu su kuma nemi abincin da suke ci.