Publicidade

Isaías 25

Yabo ga Ubangiji

1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka,

gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki,

abubuwan da aka shirya tun da.

2 Ka mai da birnin tsibin tarkace,

ka lalatar da gari mai katanga,

birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.

3 Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka;

biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.

4 Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa,

wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana.

Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango

5 kuma kamar zafin hamada.

Ka kwantar da hayaniyar baƙi;

kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.

6 A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane,

liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.

7 A wannan dutse zai kawar da

baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane,

ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;

8 zai haɗiye mutuwa har abada.

Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye

daga dukan fuskoki;

zai kawar da kunyar mutanensa

daga dukan duniya.

Ubangiji ne ya faɗa.

9 A wannan rana za su ce,

"Tabbatacce wannan shi ne Allah;

mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu.

Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi;

bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa."

10 Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse;

amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa

kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.

11 Za su buɗe hannuwansa a cikinsa,

yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo.

Allah ya ƙasƙantar da girmankansu

duk da wayon hannuwansu.

12 Zai rurrushe manyan katangar kagaru

ya kuma ƙasƙantar da su;

zai rushe su har ƙasa,

su zama ƙura.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-18_09-43-29-