Publicidade

Apocalipse 19

Halleluya sau uku a kan fāɗuwar Babilon

1 Bayan wannan sai na ji abin da ya yi kamar ƙasaitaccen taron mutane a sama, suna cewa,

"Halleluya!

Ceto da ɗaukaka da iko sun tabbata ga Allahnmu,

2 gama hukuncinsa daidai ne, mai adalci kuma.

Ya hukunta babbar karuwan nan

wadda ta ɓata duniya da zinace zinacenta.

Ya rama jinin bayinsa a kanta."

3 Suka sāke da murya suka ce,

"Halleluya!

Hayaƙin yake fitowa daga wurinta ya yi ta tashi sama har abada abadin."

Veja também

Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-07-05_19-25-13-