Halleluya sau uku a kan fāɗuwar Babilon
1 Bayan wannan sai na ji abin da ya yi kamar ƙasaitaccen taron mutane a sama, suna cewa,
"Halleluya!
Ceto da ɗaukaka da iko sun tabbata ga Allahnmu,
2 gama hukuncinsa daidai ne, mai adalci kuma.
Ya hukunta babbar karuwan nan
wadda ta ɓata duniya da zinace zinacenta.
Ya rama jinin bayinsa a kanta."
3 Suka sāke tā da murya suka ce,
"Halleluya!
Hayaƙin yake fitowa daga wurinta ya yi ta tashi sama har abada abadin."