36 Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a. 37 Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba. 38 Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.