30 Sai Filibus ya ruga zuwa wajen keken yaƙin ya kuma ji mutumin yana karatun littafin annabin Ishaya. Filibus ya yi tambaya ya ce, "Ka fahimci abin da kake karantawa?"
31 Sai ya ce, "Ina fa zan iya, in ba dai wani ya fassara mini ba?" Saboda haka sai ya gayyaci Filibus yă hau yă zauna tare da shi.
32 Bābān yana karanta wannan Nassin,
"An ja shi kamar tunkiya zuwa mayanka,
kuma kamar ɗan rago a hannun mai askin gashinsa yake shiru,
haka kuwa bai buɗe bakinsa ba.