6 Abram ya ce, "Baiwarki tana a hannunki? Ki yi da ita yadda kika ga ya fi kyau." Sai Saira ta wulaƙanta Hagar; saboda haka ta gudu daga gare ta.
7 Mala’ikan Ubangiji ya sami Hagar kusa da maɓulɓula a jeji, ita ce maɓulɓular da take gefen hanya zuwa Shur. 8 Ya kuma ce mata, "Hagar, baiwar Saira, daga ina kika fito, kuma ina za ki?"
Ta amsa ta ce, "Ina gudu ne daga wurin uwargijiyata Saira."