23 Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, "Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta? 24 Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba? 25 Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?"
26 Ubangiji ce, "In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su."
27 Sai Ibrahim ya ƙara cewa, "Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka, 28 in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?"
Ya ce, "In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba."
29 Ya sāke cewa, "In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?"
Ya ce, "Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba."
30 Sai ya ce, "Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?"
Ya ce, "Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can."
31 Ibrahim ya ce, "Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?"
Ya ce, "Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba."
32 Sa’an nan Ibrahim ya ce, "Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?"
Ubangiji ya ce, "Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba."
33 Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.