45 Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, "Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf."
46 Natanayel ya ce, "A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?"
Filibus ya ce, "Zo ka gani."