21 Sai Marta ta ce wa Yesu, "Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba. 22 Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa."
23 Yesu ya ce mata, "Ɗan’uwanki zai sāke tashi."
24 Marta ta amsa ta ce, "Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe."
25 Yesu ya ce mata, "Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu; 26 kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?"
27 Sai ta ce masa, "I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya."