Pular para o conteúdo
Publicidade

Lucas 1

Annabcin haihuwar Yesu

26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili, 27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu. 28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, "A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke."

29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka? 30 Amma mala’ikan ya ce mata, "Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah. 31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu. 32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda, 33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba."

34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, "Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?"

35 Mala’ikan ya amsa ya ce, "Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi1.35 Ko kuwa Saboda haka, yaron da za a haifa za a kira shi mai tsarki Ɗan Allah. 36 Yar’uwarki Elizabet ma za haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida. 37 Gama ba abin da zai gagari Allah."

38 Maryamu ta amsa ta ce, "To, ni baiwar Allah ce, bari zama mini kamar yadda ka faɗa." Sai mala’ikan ya tafi abinsa.

Veja também