25 To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi. 26 An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji. 27 Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci, 28 sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29 "Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari,
yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30 Gama idanuna sun ga cetonka,
31 wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32 haske don bayyanawa ga Al’ummai
da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila."