Pular para o conteúdo
Publicidade

Firistoci 16

Ranar kafara

1 Ubangiji ya yi magana da Musa bayan mutuwar ya’yan Haruna biyu maza waɗanda suka mutu sa’ad da suka kusaci Ubangiji. 2 Ubangiji ya ce wa Musa, "Faɗa wa ɗan’uwanka Haruna, kada riƙa shiga Wuri Mafi Tsarki bayan labule koyaushe, wato, a gaban murfi wanda yake bisa akwatin alkawari, domin kada mutu, gama zan bayyana a cikin girgije a kan murfin.

3 "Ga yadda Haruna zai shiga wuri mai tsarki, zai zo da ɗan bijimi domin hadaya don zunubi da kuma rago domin hadaya ta ƙonawa. 4 Zai sa toguwar lilin mai tsarki, tare da ɗan ciki na lilin; zai yi ɗamara da igiya kewaye da shi, kuma sa hular lilin. Waɗannan su ne riguna masu tsarki; saboda haka dole yi wanka kafin sa su. 5 Zai ɗauki bunsurai biyu daga jama’ar Isra’ilawa na hadaya don zunubi da ɗan rago don hadaya ta ƙonawa.

6 "Haruna zai miƙa bijimi hadaya don zunubinsa kuma yi kafara don kansa da gidansa. 7 Sa’an nan zai ɗauki bunsurai biyu miƙa su a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. 8 Haruna zai jefa ƙuri’a don awaki biyun ɗin, ƙuri’a ɗaya domin Ubangiji, ɗayan kuma don azazel16.8 Wato, akuya don cirewa; Ibraniyanci azazel, haka ma a ayoyi 10 da 26. 9 Haruna zai kawo akuyar da ƙuri’a ta fāɗi a kai wa Ubangiji miƙa ta na hadaya don zunubi. 10 Amma za a miƙa akuyar da aka zaɓa ta wurin ƙuri’a a matsayi ta azazel da rai a gaban Ubangiji don a yi amfani da ita don kafara ta wurin korinta zuwa cikin jeji kamar azazel.

11 "Haruna zai kawo bijimi domin hadayarsa ta zunubi don yi kafara wa kansa da kuma domin gidansa, zai kuma yanka bijimin domin nasa hadaya don zunubi. 12 Zai ɗauki faranti cike da garwashin wuta daga bagade a gaban Ubangiji, kuma cika hannunsa biyu da turare mai ƙanshin da aka niƙa kai su bayan labule. 13 Zai sa turaren a wuta a gaban Ubangiji, hayaƙin turaren kuwa zai rufe murfin kafarar a bisa Akwatin Alkawari, don kada mutu. 14 Zai ɗibi jinin bijimin da yatsarsa yayyafa a gaban murfin kafarar; sa’an nan yayyafa jinin da yatsarsa sau bakwai a gaban murfin kafarar.

15 "Sa’an nan zai yanka akuya na hadaya don zunubi saboda mutane, kai jinin bayan labule, yi da shi yadda ya yi da jinin bijimin. Zai yayyafa shi a kan murfin kafarar da kuma a gabansa. 16 Ta haka zai yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki saboda ƙazantar tawayen Isra’ilawa, da laifofinsu, da dukan zunubansu. Haka zai yi saboda Tentin Sujada wanda yake a cikinsu a tsakiyar ƙazantarsu. 17 Kada kowa kasance a Tentin Sujada daga lokacin da Haruna ya shiga don yi kafara a Wuri Mafi Tsarki har sai ya fita, bayan ya yi kafara domin kansa, gidansa da kuma dukan jama’ar Isra’ila.

18 "Sa’an nan zai fita zuwa bagade da yake a gaban Ubangiji, yi kafara dominsa. Zai ɗibi jinin bijimi da na akuya zuba a ƙahonin bagade. 19 Zai yayyafa jinin a kan bagade da yatsarsa sau bakwai, tsabtacce shi kuma tsarkake shi daga ƙazantar Isra’ilawa.

20 "Sa’ad da Haruna ya gama yin kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da kuma bagade, sai kawo akuya mai rai. 21 Haruna zai ɗibiya hannuwansa a kan akuya mai ran, furta a kansa dukan mugunta da tawayen Isra’ilawa, dukan zunubansu, kuma sa su a kan akuyan. Zai kori akuyan zuwa cikin jeji a hannun mutumin da aka ba shi aikin yin haka. 22 Akuyan zai ɗauka a kansa dukan zunubansu zuwa kaɗaitaccen wuri, a can mutumin zai sake shi a jeji.

23 "Sa’an nan Haruna zai shiga Tentin Sujada tuɓe rigunansa na lilin da ya sa, kafin shiga Wuri Mafi Tsarki, zai kuma bar su a can. 24 Zai yi wanka a tsattsarkan wuri sa rigunarsa na kullum. Sa’an nan zai fita miƙa hadaya ta ƙonawa domin kansa da hadaya ta ƙonawa domin mutane, don yi kafara domin kansa da kuma domin mutane. 25 Zai kuma ƙone kitsen hadaya don zunubi a kan bagade.

26 "Dole mutumin da ya saki akuya na azazel wanke rigunansa kuma yi wanka; bayan haka zai iya shiga sansani. 27 Dole a ɗauki jini, fata, nama da kuma ƙashin bijimi da akuyan hadaya don zunubi, waɗanda aka kawo jininsu cikin Wuri Mafi Tsarki don kafara, a kai waje da sansani a ƙone. 28 Dole mutumin da ya ƙone su wanke rigunansa kuma yi wanka, bayan haka zai iya shiga sansani.

29 "Wannan za zama dawwammamiyar farilla a gare ku. A rana ta goma ga wata na bakwai, dole ku yi mūsu kanku,16.29 Ko kuwa dole ku yi azumi; haka ma a aya 31. ba kuwa za ku yi wani aiki ba, ko da mutum baƙo ne a cikinku ko kuwa ɗan ƙasa, 30 gama a wannan rana za a yi kafara dominku, don a tsarkake ku. Sa’an nan a gaban Ubangiji, za a tsarkake ku daga dukan zunubanku. 31 Asabbaci ne don hutawa, kuma dole ku yi mūsun kanku; wannan dawwammamiyar farilla ce. 32 Firist da aka keɓe aka kuma naɗa don gāji mahaifinsa a matsayin babban firist ne zai yi kafara. Zai sa rigunan lilin masu tsarki 33 yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da bagade, da kuma saboda firistoci da kuma dukan jama’ar Isra’ila.

34 "Wannan za zama dawwammamiyar farilla ce gare ku. Za a riƙa yin kafara sau ɗaya a shekara saboda dukan zunuban Isra’ilawa."

Aka kuma yi haka, yadda Ubangiji ya umarci Musa.

Estes versículos te tocaram? Ore agora!

+581 estão orando agora.

Junte-se à corrente de oração.

Veja também