17 Gama Hiridus da kansa ya ba da umarni a kama Yohanna, ya kuma sa aka daure shi, aka sa shi a kurkuku. Ya yi haka saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus, wadda ya aura. 18 Gama Yohanna ya yi ta ce wa Hiridus, "Ba daidai ba ne bisa ga doka, ka ɗauki matar ɗan’uwanka."