Pular para o conteúdo
Publicidade

Mattiyu 15

3 Yesu ya amsa ya ce, "Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku? 4 Gama Allah ya ce, Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,15.4 Fit 20.12; M Sh 5.16 kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.15.4 Fit 21.17; Fir 20.9 5 Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, Duk taimakon da ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah, 6 ba zai girmama mahaifinsada shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku. 7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,

8 " Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni,

amma zukatansu suna nesa da ni.

9 A banza suke mini sujada,

koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’ " 15.9 Ish 29.13

Veja também