Pular para o conteúdo
Publicidade

Mateus 19

23 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, "Gaskiya nake gaya muku, yana da wuya mai arziki shiga mulkin sama. 24 Har wa yau ina gaya muku, zai fi sauƙi raƙumi shiga ta kafar allura, da mai arziki shiga mulkin Allah."

25 Sa’ad da almajiran suka ji wannan, sai suka yi mamaki ƙwarai. Suka yi tambaya suka ce, "To, wa zai sami ceto ke nan?"

26 Yesu ya kalle su ya ce, "Ga mutum kam, wannan ba ya yiwuwa, amma ga Allah kuwa, dukan abubuwa masu yiwuwa ne."

Veja também