Pular para o conteúdo
Publicidade

Mateus 9

Yesu ya warkar da makafi da kuma kurame

27 Da Yesu ya fita daga can, sai waɗansu makafi biyu suka bi shi, suna kira, suna cewa, "Ka yi mana jinƙai, Ɗan Dawuda!"

28 Da ya shiga cikin gida, sai makafin nan suka zo wurinsa, ya kuma tambaye su, "Kun gaskata cewa ina iya yin wannan?"

Suka amsa suka ce, "I, Ubangiji."

29 Sa’an nan ya taɓa idanunsu ya ce, "Bisa ga bangaskiyarku a yi muku haka"; 30 sai idanunsu suka buɗe. Yesu ya gargaɗe su sosai ya ce, "Ku lura kada wani san wani abu game da wannan." 31 Amma suka fita suka yi ta baza labari game da shi ko’ina a wannan yankin.

Veja também