Publicidade

Naum 3

Kaiton Ninebe

1 Kaiton birni mai zub da jini,

wadda take cike da ƙarairayi,

cike da ganima,

wadda ba a rasa masu fāɗawa cikin wahala!

2 Ku ji karar bulala

da kwaramniyar ƙafafu,

da sukuwar dawakai

da girgizar kekunan yaƙi!

3 Mahaya dawakai sun kunno kai,

takuba suna walƙiya,

māsu kuma suna ƙyali;

ga ɗumbun da aka kashe

ga tsibin matattu,

gawawwaki ba iyaka,

mutane suna tuntuɓe da gawawwaki,

4 duk saboda yawan sha’awace-sha’awacen karuwa,

mai daɗin baki, uwargidan maita,

wadda ta ɓad da al’ummai ta wurin karuwancinta

ta kuma ɓad da mutane ta wurin maitancinta.

5 "Ina gāba da ke," in ji Ubangiji Maɗaukaki.

"Zan kware fatarinki a idonki.

Zan nuna wa al’ummai tsiraicinki,

masarautai kuma kunyarki.

6 Zan watsa miki ƙazanta,

in yi miki wulaƙanci

in kuma mai da ke abin reni.

7 Duk wanda ya gan ki zai gudu daga gare ki yana cewa,

‘Ninebe ta lalace, wa zai yi makoki domin ta?’

Ina zan sami wani wanda zai yi miki ta’aziyya?"

8 Kin fi Tebes ne

da take a bakin Nilu,

da ruwa yake kewaye da ita?

Rafi shi ne kāriyarta,

ruwanta kuma katanga.

9 Kush da kuma Masar su ne ƙarfinta marar iyaka;

Fut da Libiya suna cikin mataimakanta.

10 Duk da haka an tafi da ita

ta kuma tafi bauta.

Aka fyaɗa ƙanananta da ƙasa

aka yayyanka su gunduwa-gunduwa a kan kowane titi.

Aka jefa ƙuri’a a kan manyan mutanenta,

aka daure manyan mutanenta da sarƙoƙi.

11 Ke ma za ki bugu,

za ki ɓuya.

Ki kuma nemi mafaka daga wurin abokin gāba.

12 Dukan kagarunki suna kama da itatuwan ɓaure

da ’ya’yansu da suka nuna.

Da an girgiza,

sai ɓaure su zuba a bakin mai sha.

13 Dubi mayaƙanki,

duk mata ne!

Ƙofofin ƙasarki

a buɗe suke ga abokan gābanki,

wuta ta cinye madogaransu.

14 Ki ja ruwa gama za a kewaye ki da yaƙi.

Ki ƙara ƙarfin kagaranki!

Ki kwaɓa laka,

ki sassaƙa turmi

ki gyara abin yin tubali!

15 A can wuta za tă cinye ki;

takobi zai sare ki,

kuma kamar fāra, za a cinye ki.

Ki riɓaɓɓanya kamar fāra,

ki riɓaɓɓanya kamar fārin ɗango!

16 Kin ƙara yawan masu kasuwancinki

har sai da suka fi taurarin sama.

Amma kamar fāra sun cinye ƙasar

sa’an nan suka tashi, suka tafi.

17 Masu tsaronki suna kama da fāri ɗango,

shugabanninki sun yi cincirindo kamar fārin ɗango

da suka sauka a kan bango a rana mai sanyi,

amma da rana ta fito, duk za su tashi su tafi,

ba kuma wanda ya san inda suka nufa.

18 Ya sarkin Assuriya, makiyayanka sun yi barci;

manyan mutanenka sun kwanta su huta.

An watsar da mutanenka a cikin duwatsu,

ba wanda zai tattaro su.

19 Ba abin da zai warkar da rauninka;

rauninka ya yi muni.

Duk wanda ya ji labarinka

zai tafa hannuwansa saboda farin cikin fāɗuwarka,

gama wane ne bai ji

jiki a hannunka ba?

Veja também

Publicidade
Naum
Ver todos os capítulos de Naum
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-18_10-32-54-