Hikima ce mafi girma duka
1 Ku saurara ’ya’yana ga koyarwar mahaifinku;
ku mai da hankali, ku sami fahimi.
2 Ina ba ku sahihiyar koyarwa,
saboda haka kada ku ƙyale koyarwata.
3 Sa’ad da nake yaro a gidan mahaifina,
yaro kaɗai kuma na mahaifiyata,
4 ya koya mini ya ce,
"Ka riƙe kalmomina da dukan zuciyarka;
ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu.
5 Ka nemi hikima, ka nemi fahimi;
kada ka manta da kalmomina ko ka kauce daga gare su.
6 Kada ka ƙyale hikima, za tă kuwa tsare ka;
ka ƙaunace ta, za tă kuwa lura da kai.