7 Sa’an nan Yusuf ya shigar da Yaƙub mahaifinsa, ya gabatar da shi a gaban Fir’auna. Bayan Yaƙub ya albarkaci47.7 Ko kuwa gai da Fir’auna, 8 sai Fir’auna ya tambaye shi, "Shekarunka nawa da haihuwa?"
9 Yaƙub kuwa ya ce wa Fir’auna, "Shekarun hijirata, shekaru ɗari da talatin ne. Shekaruna kaɗan ne cike da wahala, ba za a kuwa daidaita su da shekarun hijirar kakannina ba." 10 Sai Yaƙub ya albarkaci47.10 Ko kuwa ya yi bankwana da Fir’auna, ya yi masa bankwana, sa’an nan ya fita.
11 Ta haka Yusuf ya zaunar da mahaifinsa da ’yan’uwansa a Masar, ya ba su mallaka a sashe mafi kyau na ƙasar, a yankin nan na Rameses, kamar yadda Fir’auna ya umarta. 12 Yusuf ya kuma tanada wa mahaifinsa da kuma ’yan’uwansa da dukan gidan mahaifinsa, abinci bisa ga yawan ’ya’yansu.