Yesu ya tsabtacce haikali
12 Kashegari, da suke barin Betani, Yesu kuwa ya ji yunwa. 13 Da ya hangi wani itacen ɓaure mai ganye, sai ya je domin yă ga ko yana da ’ya’ya. Amma da ya kai can, bai tarar da kome ba sai ganye, domin ba lokacin ’ya’yan ɓaure ba ne. 14 Sai ya ce wa itacen, "Kada kowa yă ƙara cin ’ya’yanka." Almajiransa kuwa suka ji ya faɗi haka.