Publicidade

Sofonias 3

Nan gaba na Urushalima

1 Taki ta ƙare, ke birnin mai danniya,

mai ’yan tawaye da kuma masu ƙazanta!

2 Ba kya yi wa kowa biyayya,

ba kya kuma yarda da kuskurenki.

Ba kya dogara ga Ubangiji,

ba kya kuma kusatowa kusa da Allahnki.

3 Sarakunanki ruri ne na zakoki,

shugabanninki kyarketan dare ne,

waɗanda ba sa rage kome don safe.

4 Annabawanki mahaukata ne

mutanenki masu cin amana ne.

Firistocinki suna ƙazantar da Wurin Mai Tsarki

suna kuma keta dokoki.

5 Ubangiji da yake cikinki mai adalci ne;

ba ya yin abin da ba daidai ba.

Kowace safiya yakan bayyana dokokinsa a fili,

kowace sabuwar rana kuma ba ya kāsawa,

duk da haka marasa adalci ba sa jin kunya.

6 "Na daddatse al’ummai;

an kuma rurrushe kagararsu.

Na bar titunansu ba kowa,

ba mai ratsawa a ciki.

An ragargaza biranensu;

ba wanda za a bari, babu ko ɗaya.

7 Na ce wa birnin,

‘Tabbatacce za ki ji tsorona

ki kuma yarda da gyara!’

Ta haka ba za a datse wurin zamanki ba,

ba kuwa dukan hukuncena za su hau bisa kansu ba.

Amma har yanzu suna marmari

su yi rashin gaskiya a duk abin da suke yi.

8 Saboda haka ku jira ni," in ji Ubangiji;

"a ranar da zan tsaya in ba da shaida,

Na yanke shawara in tattara dukan al’ummai,

in tattara mulkoki

in kuma zuba fushina a kansu,

da dukan zafin haushina.

Za a mamaye dukan duniya

da zafin fushina.

9 "Sa’an nan zan tsarkake leɓunan mutanen,

don dukansu su kira bisa ga sunan Ubangiji

su kuma yi masa hidima kafaɗa da kafaɗa.

10 Tun daga ƙetaren rafuffukan Kush

masu yi mini sujada, mutanena da suke a warwatse,

za su kawo mini hadayu.

11 A wannan rana ba za ku sha kunya

saboda laifofin da kuka yi mini,

gama zan ɗauke wa wannan birni

waɗanda suke farin ciki cikin girmankansu.

Ba kuma za ka ƙara yin kallon reni

a tuduna mai tsarki ba.

12 Amma zan zauna a cikinki

masu tawali’u da masu ƙasƙantar da kai,

waɗanda suke dogara ga sunan Ubangiji.

13 Raguwar Isra’ila ba za su ƙara aikata abin da ba daidai ba,

ba za su faɗa ƙarya ba,

ba kuwa za a sami ruɗu a bakunansu ba.

Za su ci su kuma kwanta

kuma babu wanda zai ba su tsoro."

14 Ki rera, ya Diyar Sihiyona;

ki tā da murya, ya Isra’ila!

Ki yi murna ki kuma yi farin ciki da dukan zuciyarki,

Ya Diyar Urushalima!

15 Ubangiji ya ɗauke hukuncinki,

ya mai da abokan gābanki baya.

Ubangiji, Sarkin Isra’ila, yana tare da ke;

ba kuma za ki ƙara jin tsoron wani lahani ba.

16 A wannan rana za su cewa Urushalima,

"Kada ki ji tsoro, ya Sihiyona;

kada ki bar hannuwanki su raunana.

17 Ubangiji Allahnki yana tare da ke,

mai iko ne don ceto.

Zai yi matuƙar farin ciki da ke,

zai rufe ki da ƙaunarsa,

zai yi farin ciki da ke ta wurin rerawa."

18 "Zan cire taƙaici daga gare ki

a ƙayyadaddun bukukkuwa;

su kaya ne da kuma zargi a gare ki.

19 A wannan lokaci zan jijji wa

waɗanda suka danne ku;

zan kuɓutar da guragu

in kuma tattara waɗanda suke a warwatse.

Zan sa a yabe su a kuma girmama su

a kowace ƙasar da aka kunyatar da su.

20 A wannan lokaci zan tattara ku;

a wannan lokaci zan kawo ku gida,

zan sa a yabe ku a kuma girmama ku

a cikin dukan mutanen duniya

a sa’ad da na maido da arzikinku

a idanunku,"

in ji Ubangiji.

Veja também

Publicidade
Sofonias
Ver todos os capítulos de Sofonias
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-18_12-43-22-