Publicidade

Amós 9

Za a hallaka Isra’ila

1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce,

"Bugi kan ginshiƙan

don madogaran ƙofa su girgiza.

Saukar da su a kan dukan mutane;

waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi.

Ba mutum guda da zai tsere,

babu wani da zai tsira.

2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari,

daga can hannuna zai fitar da su.

Ko da sun hau can sama

daga can zan sauko da su.

3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel,

a can zan farauce su in cafko.

Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku,

a can zan umarci maciji sare su.

4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta,

a can zan umarci takobi kashe su.

"Zan sa musu ido

don mugunta ba don alheri ba."

5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki,

shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke,

kuma dukan mazauna cikinta suna makoki,

ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu,

sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,

6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa9.6 Ma’anar Ibraniyanci don wannan zance babu tabbas. a cikin sammai

ya kuma kafa harsashenta9.6 Ma’anar Ibraniyanci don wannan kalma babu tabbas. a duniya,

shi da yakan kira ruwan teku

kuma kwarara su a bisa duniya,

Ubangiji ne sunansa.

7 "Ku ba Isra’ilawa ba ne,

daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?"9.7 Wato, mutane daga yankin bisa na Nilu

In ji Ubangiji.

"Ban fito da Isra’ila daga Masar ba,

Filistiyawa kuma daga Kaftor9.7 Wato, Kirit

Arameyawa kuma daga Kir ba?

8 "Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka

suna a kan mulkin nan mai zunubi.

Zan hallaka shi

daga fuskar duniya,

duk da haka ba zan hallaka

gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,"

in ji Ubangiji.

9 "Gama zan ba da umarni,

zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila

a cikin dukan ƙasashe

kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi

kuma ko ƙwaya ɗaya ba za fāɗi a ƙasa ba.

10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena

za su mutu ta wurin takobi,

wato, su masu cewa,

Masifa ba za fāɗo ko ta same mu ba.

Maidowar Isra’ila

11 "A wannan rana zan maido

da tentin Dawuda da ya fāɗi.

Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage,

in kuma maido da kufansa

in gina shi kamar yadda yake a ,

12 domin su mallaki raguwar Edom

da duk al’ummai da suke amsa sunana,"9.12 Da Ibraniyanci; Seftuwajin don raguwar mutane / da kuma dukan al’umman da ake kira da sunana za su nemi Ubangiji

in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.

13 "Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji,

"sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi

mai shuki kuma bi bayan mai matsin inabi.

Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu

kuma kwararo daga tuddai.

14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta9.14 Ko kuwa zan maido da nasarar mutanena Isra’ila.

"Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu.

Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu;

za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.

15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu,

ba kuwa za a ƙara tumɓuke su

daga ƙasar da na ba su ba,"

in ji Ubangiji Allahnku.

Veja também

Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-07-05_19-25-13-