Ayuba
1 Sai Ayuba ya amsa,
2 "Lalle, na san wannan gaskiya ne.
Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi,
ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa.
Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?