Pular para o conteúdo
Publicidade

Números 6

Banazare

1 Ubangiji ya ce wa Musa, 2 "Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, In mace, ko namiji yana so yi alkawari na musamman, alkawarin zaman keɓaɓɓe ga Ubangiji, a matsayin Banazare, 3 dole keɓe kansa daga ruwan inabi, ko daga waɗansu abubuwa sha masu sa maye, kada kuma sha ruwan tsamin da aka yi daga ruwan inabi, ko daga waɗansu abubuwa sha masu sa maye. Ba zai sha ruwan ya’yan inabi, ko ci ya’yan inabi ɗanye ko busasshe ba. 4 Muddin yana Banazare, ba zai ci wani abin da ya fito daga ya’yan inabi ba, ko ƙwayar inabi, ko ɓawonsa ma.

5 " A dukan lokacin da yake a kan alkawarin keɓewarsa, reza ba zai taɓa kansa. Dole kasance da tsarki har ƙarshen keɓewarsa ga Ubangiji; tilas bar gashin kansa yi tsawo. 6 A dukan kwanakin keɓewarsa ga Ubangiji, Banazarin ba zai yi kusa da gawa ba. 7 Ko da ma gawar ta mahaifinsa ce, ko ta mahaifiyarsa, ko ta ɗan mahaifiyarsa, ko kuma ta yar’uwarsa ce, ba zai ƙazantar da kansa saboda su ba, domin alamar keɓewarsa ga Allah tana kansa. 8 A dukan kwanakin keɓewarsa, an tsarkake shi ga Ubangiji.

9 " In farat ɗaya wani ya mutu kusa da shi, to, keɓewarsa ta ƙazantu, dole aske kansa a ranar tsarkakewarsa, a rana ta bakwai. 10 Sa’an nan a rana ta takwas, tilas kawo wa firist yan kurciyoyi biyu, ko kuma yan tattabarai biyu a bakin ƙofar Tentin Sujada. 11 Firist kuwa zai miƙa ɗaya don hadaya ta zunubi, ɗayan kuma don hadaya ta ƙonawa, yi kafara dominsa, gama ya yi zunubi ta dalilin gawar. A wannan rana zai sāke keɓe kansa. 12 Dole keɓe kansa ga Ubangiji, har kwanakin keɓewarsa, kuma dole kawo ɗan rago bana ɗaya a matsayin hadayar laifi. Kwanakin baya ba sa cikin lissafi, domin ya ƙazantu a lokacin keɓewarsa.

13 " To, ga doka saboda Banazare sa’ad da kwanakin keɓewarsa suka gama. Za a kawo shi a bakin ƙofar Tentin Sujada. 14 A can zai miƙa hadayunsa ga Ubangiji. Hadayun kuwa su ne, ɗan rago, bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa, yar tunkiya, bana ɗaya marar lahani na hadaya don zunubi, rago marar lahani don hadaya ta salama, 15 tare da hadayu na hatsi da hadayu na sha, da kuma kwando burodi marar yisti, ƙosai da aka yi da lallausan gari kwaɓaɓɓe da mai, da kuma wainan da aka barbaɗa da mai.

16 " Firist zai kawo su a gaban Ubangiji, miƙa hadaya don zunubi da hadaya ta ƙonawa. 17 Zai miƙa kwandon burodi marar yisti, kuma miƙa ɗan ragon hadaya ta salama tare da hadaya ta gari, da hadaya ta sha ga Ubangiji.

18 " Sa’an nan a ƙofar Tentin Sujada, dole Banazaren aske gashin da ya alamta keɓewarsa, kwashe gashin, zuba a cikin wutar da take ƙarƙashin hadaya ta salama.

19 " Bayan Banazaren ya aske gashinsa da ya alamta keɓewa, firist zai ɗauki dafaffiyar kafaɗar rago, da ƙosai da kuma waina daga cikin kwando waɗanda duka biyu marar yisti ne, sa su a tafin hannun keɓaɓɓen. 20 Firist zai kaɗa su a gaban Ubangiji, hadaya ce ta kaɗawa; mai tsarki ne kuma, zai zama na firist, tare da ƙirjin da aka kaɗa da kuma cinyar da aka kawo. Bayan haka, Banazaren zai iya shan ruwan inabi.

21 " Wannan ita ce dokar Banazare wanda ya yi alkawari ga Ubangiji bisa ga keɓewarsa, tare da duk abin da zai iya bayarwa. Tilas cika alkawarin da ya yi bisa ga dokar zaman Banazare.’ "

Albarkar da firist zai sa wa jama’a

22 Ubangiji ya ce wa Musa, 23 "Gaya wa Haruna da ya’yansa, Ga yadda za ku albarkaci Isra’ilawa. Za ku ce musu,

24 " ‘ "Ubangiji albarkace ku,

kuma kiyaye ku;

25 Ubangiji sa fuskarsa ta haskaka a kanku,

kuma yi muku alheri;

26 Ubangiji dube ku da idon rahama,

kuma ba ku salama." 

27 "Da haka za su sa sunana a kan Isra’ilawa, ni kuma zan albarkace su."

Veja também