Pular para o conteúdo
Publicidade

Irmiya 24

Kwanduna biyu na ya’yan ɓaure

1 Bayan Nebukadnezzar ya kwashi Yekoniya24.1 Da Ibraniyanci Yekoniya, wani suna na Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da fadawa, da masu sana’a da masu zane zanen Yahuda daga Urushalima zuwa Babilon zaman bauta, Ubangiji ya nuna mini kwanduna biyu na ya’yan ɓaure ajiye a gaban haikalin Ubangiji. 2 Kwando guda yana da ya’yan ɓaure masu kyau sosai, kamar waɗanda suka nuna da wuri; ɗayan kwandon kuma yana da ya’yan ɓaure marasa kyau, sun yi muni har ba a iya ci.

3 Sa’an nan Ubangiji ya tambaye ni ya ce, "Me ka gani, Irmiya?"

Na ce, "Ya’yan ɓaure. Masu kyau ɗin suna da kyau sosai, amma munanan sun yi muni har ba a iya ci."

4 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa, 5 "Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, Kamar ya’yan ɓauren nan masu kyau, haka zan kula da mutanen Yahuda waɗanda aka kwaso waɗanda na fisshe su daga wannan wuri zuwa ƙasar Babiloniyawa24.5 Ko kuwa Kaldiyawa 6 Idanuna za su kula da su don kyautatawarsu, zan kuma komo da su wannan ƙasa. Zan gina su ba zan rushe su ba; zan dasa su ba kuwa zan tumɓuke su ba. 7 Zan ba su zuciya don su san ni, cewa ni ne Ubangiji. Za su zama mutanena, zan zama Allahnsu, gama za su komo gare ni da dukan zuciyarsu.

8 " Amma kamar ya’yan ɓauren nan marasa kyau, waɗanda sun yi muni har ba a iya ci,in ji Ubangiji, haka zan yi da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da sauran mutanen da suka tsira a Urushalima, ko suna a wannan ƙasa ko suna zama a Masar. 9 Zan mai da su abin ƙyama da masifa ga dukan mulkokin duniya, abin zargi da abin karin magana, abin ba’a da abin la’ana a duk inda zan kore su zuwa. 10 Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu sai an hallaka su sarai daga ƙasar da na ba su da kuma kakanninsu.’ "

Estes versículos te tocaram? Ore agora!

+581 estão orando agora.

Junte-se à corrente de oração.

Veja também