31 "Lokaci yana zuwa," in ji Ubangiji,
"sa’ad da zan yi sabon alkawari
da gidan Isra’ila
da kuma gidan Yahuda.
32 Ba zai zama kamar alkawarin
da na yi da kakanni kakanninsu ba
sa’ad da na kama su da hannu
na bishe su daga Masar,
domin sun take alkawarina,
ko da yake na zama miji a gare su,"
in ji Ubangiji.
33 "Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila
bayan wannan lokaci," in ji Ubangiji.
"Zan sa dokata a tunaninsu
in kuma rubuta ta a zukatansu.
Zan zama Allahnsu,
za su kuma zama mutanena.