Publicidade

Oséias 14

Tuba don kawo albarka

1 Ku dawo, ya Isra’ila, ga Ubangiji Allahnku.

Zunubanku ne sun zama sanadin fāɗuwarku!

2 Ku ɗauki magana tare da ku

ku komo wurin Ubangiji.

Ku ce masa,

"Ka gafarta mana dukan zunubanmu

ka kuma karɓe mu da alheri,

don mu iya yabe ka da leɓunanmu.

3 Assuriya ba za su iya cece mu ba;

ba za mu hau dawakan yaƙi ba.

Ba za mu ƙara ce, ‘Allolinmu’

wa abin da hannuwanmu suka yi ba,

gama a gare ka ne maraya yakan sami jinƙai."

4 "Zan gyara ɓatancinsu

in kuma ƙaunace su a sake,

gama fushina ya juya daga gare su.

5 Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila

zai yi fure kamar lili.

Kamar al’ul na Lebanon

zai sa saiwarsa zuwa ƙasa;

6 tohonsa za su yi girma.

Darajarsa za tă zama kamar itacen zaitun,

ƙanshinsa kamar al’ul na Lebanon.

7 Mutane za su sāke zauna a inuwarsa.

Zai haɓaka kamar ƙwayar hatsi.

Zai yi fure kamar kuringa,

zai zama sananne kamar ruwan inabi daga Lebanon.

8 Efraim zai ce, me kuma zai haɗa ni da gumaka?

Zan amsa masa in kuma lura da shi.

Ni kamar koren itacen fir ne;

amincinka yana fitowa daga gare ni ne."

9 Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa.

Hanyoyin Ubangiji daidai ne;

masu adalci sukan yi tafiya a kansu,

amma ’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-18_12-43-22-