31 "Lokaci yana zuwa," in ji Ubangiji,
"sa’ad da zan yi sabon alkawari
da gidan Isra’ila
da kuma gidan Yahuda.
32 Ba zai zama kamar alkawarin
da na yi da kakanni kakanninsu ba
sa’ad da na kama su da hannu
na bishe su daga Masar,
domin sun take alkawarina,
ko da yake na zama miji a gare su,"
in ji Ubangiji.
33 "Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila
bayan wannan lokaci," in ji Ubangiji.
"Zan sa dokata a tunaninsu
in kuma rubuta ta a zukatansu.
Zan zama Allahnsu,
za su kuma zama mutanena.
34 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba,
ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’
domin duk za su san ni,
daga ƙaraminsu har zuwa babba,"
in ji Ubangiji.
"Gama zan gafarta muguntarsu
ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba."