Kaiton waɗanda suke dogara ga Masar
1 Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako,
waɗanda suke dogara ga dawakai,
waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu
da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu,
amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila,
ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
2 Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa;
ba ya janye kalmominsa.
Zai yi gāba da gidan mugu,
gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.