3 "Ku kasa kunne gare ni, ya ku gidan Yaƙub,
dukanku waɗanda kuka rage na gidan Isra’ila,
ku da na lura da ku tun da aka yi cikinku,
na kuma riƙe ku tun haihuwarku.
4 Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura
ni ne shi, ni ne shi wanda zai lura da ku.
Na yi ku zan kuma riƙe ku;
zan lura da ku
in kuma kuɓutar da ku.